Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An samu dauke wuar lantarki a sassan kasarnan sakamakon lalacewar wasu na’urori

Published

on

An samu daukewar wutar lantarki a yankunan kasar nan da dama a daren jiya Talata sakamakon lalacewar wasu na’urori a tashoshin tunkudo wutar lantarki na kasar nan.

Rahotanni sun ce gobara ce ta tashi a bututun mai da ya taso daga Escravos zuwa Lagos wanda ya yi sanadiyyar lalacewar na’urori a kamfanin tunkudo wutar lantarki.

Lamarin dai ya yi sanadiyyar lalacewar bututu guda shida a kamfanin tunkudo wutar lantarki.

Da safiyar yau ne kuma ma’aikatar samar da wutar lantarki ayyuka da gidaje ta fitar da wata sanarwa wanda kuma ya tabbatar da faruwar lamarin.

A cewar ma’aikatar lamarin ya yi sanadiyyar dakatar da aiki a tashoshin tunkudo wutar lantarki na Egbin da Olorunsogo da Omotosho da kuma Paras.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!