Connect with us

Labarai

Wata kungiyar APC ta bukaci Abdullahi Abbas ya gaggauta sauka daga mukamin sa kafin ranar biyar ga watan Yuli mai zuwa

Published

on

Kungiyar APC Kadangaren Bakin Tulu ta bukaci shugaban Jam’iyyar a nan Kano Abdullahi Abbas da ya gaggauta sauka daga mukamin shugabancin Jam’iyyar kafin nan da ranar biyar ga watan Yuli mai kamawa.

Haka zalika kungiyar ta bukaci sabon shugaban Jam’iyyar na Kasa Bukar Dalori da ya sauke shugabancin na Abdullahi Abbas a nan Kano duba da rarraba kawunan yan jam’iyyar da ya yi.

Hakan na zuwa ne a wata ganawa da shugabancin kungiyar ya yi da manema labarai a yau ta bakin Sakataren kungiyar Kwamred Abubakar Abdullahi Dangarinnan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!