Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Wata mata ta zargi makociyarta da maita a Kano

Published

on

Wata mata mai suna Rabi Muhammad mazauniyar unguwar Farawa dake nan Kano, ta zargi wata makociyar da kama kurwar ‘yar ta mai suna Shema’u.

Rabi Muhammad ta yi zargin cewa makociyar ta mai suna Tine Usman tana zuwar wa ‘yar ta Shema’u dauke da wuka a mafarki, sannan tana ikrarin kashe ta.

Akan hakan ne ya sanya wasu matasa masu fushi da fushin wani su kayi yunkurin farwa Tine Usman da ake zargi, sai dai ‘yan sanda sun kai mata dauki inda suka dakatar da yunkurin matasan.

Sakamakon hakan ne ‘yan sanda suka tura yarinyar asibiti domin ayi mata gwaje-gwaje wanda a karshe aka gano cewa babu wata maita hassalima zazzafan zazzabin Trypot da Malaria ne ke damun ta.

A karshe dai ‘yan sandan Farawa sun aika da wannan dambarwa zuwa gaban kotu, inda za a fara sauraron karar nan bada jimawa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!