Connect with us

Labarai

Yaƙin Amurka da Iran ya dagula shirin Umrah na Musulman Najeriya

Published

on

Rikicin yaƙi tsakanin Amurka da Iran ya janyo cikas ga tafiyar Umrah ta daruruwan Musulman Najeriya, bayan da kamfanonin jiragen sama suka soke tashin jirage zuwa Gabas ta Tsakiya. Lamarin ya sa mutane da dama da suka riga suka biya kuɗin biza, jirgi da masauki a Makka da Madina suka yi asarar miliyoyin naira.

Rahotanni sun nuna cewa wasu maniyyata sun shirya tashi daga Najeriya tsakanin ranar 4 zuwa 6 ga watan Maris, amma kamfanonin jiragen sama irin su Qatar Airways da Emirates sun dakatar da zirga-zirgar jirage saboda rufe wasu sararin samaniya a ƙasashen Gabas ta Tsakiya sakamakon hare-haren da aka yi a yankin.

Wasu daga cikin maniyyatan sun ce sun kashe sama da miliyoyin naira kan tafiyar Umrah tare da iyalansu, amma yanzu suna cikin damuwa domin kamfanonin jiragen sama sun ce za a iya sauya ranar tafiya ne kawai ba tare da dawo da cikakken kuɗi ba. Duk da haka, wasu da suka riga suka isa ƙasar Saudi Arabia sun ce ana gudanar da ibada lafiya, sai dai matsalar ta fi shafar zirga-zirgar jirage.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!