Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisa zata dakatar da jiragen saman Amurka da Burtaniya zuwa Najeriya

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce daga mako mai kamawa zata dakatar da zirga-zirgar jiragen sama daga wasu kasashen duniya da suka hadar da Burtaniya da Amurka zuwa Najeriya sakamakon bazuwar cutar corona a kasashen karo na biyu.

Shugaban kwamitin kula da zirga-zirgar jiragen sama na majalisar dajjitai Smart Adeyemi ne ya bayyana hakan jiya a Abuja.

Adeyemi ya ce hukuncin dakatar da zirga-zirgar zai fara ne daga mako mai kamawa sakamakon yadda ake samun karuwar masu dauke da cutar a kasashen, a don haka gwamnatin Najeriya zata sanar da matakin ta na gaba a mako mai kamawa.

Ya ce, ci gaba da shigowar baki daga kasashen zai kara yada cutar wanda a yanzu ana samun adadi mafi yawa na masu dauke da cutar a kullum.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!