Labarai
Yadda Gwamna Abba Kabir ya jagoranci zaman majalisar zartaswa a birnin Kwankwasiyya

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci zaman majalisar zartaswa na farko a sabon gidan gwamnati dake rukunin gidaje na Khalifa Isiyaka Rabi’u da a baya aka fi sani da birnin Kwankwasiyya.
Da ya ke jawabi yayin bude zaman majalisar Karo na 27, gwamna Abba Kabir Yusuf, ya ce, ya kai zaman majalisar sabon gidan hutawar gwamnati dake rukunin gidajen ne domin raya birnin da kuma janyo hankalin al’umar da suka mallaki gidaje a birnin don su tare da iyalansu.
Haka kuma, ya ce, gwamnatin jihar Kano ta samar da dukkanin abubuwan more rayuwa a rukunin gidajen da nufin kyautata rayuwar mazauna yankin.
You must be logged in to post a comment Login