Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma kusan 32 a jihar Niger

Published

on

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar Niger.

Mazauna yankin sun ce harin farko ya faru ne da misalin karfe 3:00 na asubahin ranar 14 ga Fabrairu a Tugan-Makeri, inda aka mutane 6 suka rasa rayukansu, aka kona gidaje tare da sace wasu. Daga baya da misalin karfe 6:00 na safe, maharan sun kai farmaki Konsoko da Pissa inda aka ce an hallaka karin mutane 26.

Wani mazaunin yankin, Hassan Abdullahi, ya shaida cewa ’yan bindigar sun kai sama da 200 kuma sun shafe awanni suna cin karensu babu babbaka, daga karfe 6:00 na safe zuwa kusan 10:00 na safe.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da harin Tugan-Makeri da mutuwar mutum shida, yana mai cewa jami’an tsaro sun bazama yankin domin daukar mataki da ceto wadanda aka sace, yayin da cikakken bayani kan sauran hare-haren ke jiran tabbaci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!