Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Yan bindiga sun hallaka mutane a Kano

Published

on

Rundunar’yan sanda ta jihar Kano ta tabbatar da cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun hari garin Bagwai dake nan Kano.

Kakakin rundunar’yan sanda ta jihar Kano DSP, Abdullahi Haruna Kiyawa , ya tabbatar da faruwar al’amarin, inda ya ce suna cigaba da bincike.

Rahotonni sun ce maharan sun farwa garin da harbe-harben bindiga inda suka hallaka mutane tare da raunata wasu.

‘Yan bindigar sun shiga garin na Bagwai ne cikin mota da misalin karfe 10:30 na daren jiya Litinin.

‘Yan bindigar sun hallaka  wata ‘yar  gidan da suka kai harin wadda take  jigo a jam’iyyar PDP Hajiya Balaraba Sani.

Daga nan ne kuma suka harbe wani mutum mai suna Muhammad Sani.

Karin labarai:

Operation Puff-Adder sun farwa ‘yan bindiga dadin na Ansaru a dajin Koduru a Kaduna

‘Yan bindiga sun yi awan gaba da wasu tagwaye

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!