Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yan bindiga sun hallaka mutum guda tare da sace mutum bakwai a Kaura Namoda

Published

on

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari wasu yankunan karamar hukumar Kaura Namoda inda suka hallaka mutun guda tare sace wasu mutum bakwai.

Maharan sun durfafin grin ne da karfe 11:30 na daren Juma’ar da ta gabata a daidai lokacin da ruwan sama ke sauka kamar da bakin kwarya.

Shugaban karamar hukumar ta Kaura Namoda Lawal Isah ya tabbatar da hakan ga manema labarai a jiya lahadi yana mai cewa cikin wadanda aka yi garkuwa da su har da dagacin garin da matansa uku da kuma dansa mai shekaru 13 da haihuwa.

A ranar alhamis din da ta gabata ne dai wasu maharan suka farwa karamar hukumar Tsafe inda suka kashea mutum 18, har ma shugaban kas Muhammadu Buhari ya mik sakon ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!