Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ministocin ilimi na kungiyar D8 zasu karfafa shirin inganta kiwon lafiya

Published

on

Ministocin ilimi na kungiyar kasashen D8 ciki har da Najeriya sun yanke shawarar karfafa shirinta na aiwatar da tsarin kiwon lafiya da karfafa al’umma.

Kungiyar ta D8 wadda kuma ta maida hankali ga fannin kiwon lafiya da tattalin arziki, ta sanar da hakan ne bayan kammala taronta a karon a farko na tuntubar juna a Abuja.

Kasashen da ke cikin kungiyar sun hadar da Bangladesh da Egypt da Indonesia da kuma Iran. Sauran su ne Malaysia da Pakistan da Turkiyya, sai kuma Najeriya.

Babban jami’in kungiyar Dokta Ado Muhammad, wanda kuma shi ne tsohon babban daraktan hukumar kula kiwon lafiya a matakin farko ta tarayya, ya shaida cewa sun samar da wannan tsari na kyautatawa al’umma a cikin watan Nuwamban bara, bayan cimma matsaya kan abinda ya shafi bunkasa harkokin kiwon lafiyar al’umma.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!