Labarai
Sojoji sun ceto mutane 48 daga masu garkuwa a Kaura Namoda

Dakarun Rundunar Operation Fansar Yamma sun ceto mutane 48 daga masu garkuwa a ƙauyen Magami da ke Karamar Hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara.
Wannan na cikin sanarwar da Jami’in Yaɗa Labaran Rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya fitar a jiya Lahadi.
Sanarwar ta ce ‘yan ta’addan, wadanda suka shigo yankin da babura kusan 40, sun yi awon gaba da dimbin mazauna yankin da nufin garkuwa da su, kafin dakarun su isa wurin bayan samun kiran neman agaji.
Ya ce, sojojin sun yi artabu da ‘yan ta’addan, lamarin da ya tilasta musu sakin mutanen tare da tserewa cikin daji.
Rundunar ta ce, mutum 1 ya rasu yayin artabun, yayin da wasu 2 suka samu raunukan harbin bindiga kuma aka kai su babban asibitin Kaura Namoda.
You must be logged in to post a comment Login