Connect with us

Labaran Kano

‘Yan bindiga sun sace sakataren ƙaramar hukuma a Kano

Published

on

Wasu ƴanbindiga sun kai hari gidan sakataren ƙaramar hukumar Kibiya da ke jihar Kano tare da sace shi.

 

Shugaban majalisar kansilolin ƙaramar hukumar Hon. Sabo Yusuf Usman ya shaida wa BBC cewa lamari ya faru ne ranar Juma’a da daddare a gidan sakataren da ke garin Dinya.

 

”Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:00 na dare, lokacin da sakataren ke barci a gidansa”, in ji shi.

 

Ya ci gaba da cewa lokacin da maharan suka je gidan sun tashi ɗan gidan sakataren da ke kwana a zauren waje, inda suka tilasta masa ƙwanƙwasa kofar gidan, sannan ya faɗa wa mahaifinsa cewa cikinsa na ciwo.

 

”Hakan kuwa aka yi, bayan ya ƙwanƙwasa mahaifin nasa ya ce wane ne? Sai ya ce shi ne (ɗansa), ya ce me ya faru? Sai ya ce cikinsa ne ke ciwo, nan take mahaifin ya buɗe ƙofa, daga nan maharan suka kama shi tare da ɗan nasa”, a cewar Hon Sabo.

 

Ya ƙara da cewa tuni dai jamai’an tsaro suka kai taimakon gaggawa, amma kafin zuwansu maharan sun tafi da sakataren bayan sun sako ɗan nasa.

 

A baya dai ba a san ƙaramar hukumar Kibiya da matsalar tsaro ba, amma an sha samun matsalolin hare-haren ƴanbindiga a ƙananan hukumomin Tsanyawa da Shanono da suka yi iyaka da jihar Katsina.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!