Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun sace tsohon dan Majalisa

Published

on

’Yan bindiga sun sace tsohon ɗan majalisar dokokin jihar Ogun, Moruf Musa, a garin Ibiade da ke ƙaramar hukumar Ogun Waterside, a ranar Talata.

Moruf Musa, wanda ya taɓa rike muƙamin Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Jihar Ogun daga shekarar 2007 zuwa 2011, an rawaito cewa an sace shi da misalin ƙarfe 7:00 na yamma, yayin da yake gudanar da sallar Magariba a masallacin da ke cikin gidansa.

Shugaban ƙaramar hukumar Ogun Waterside, Ganiyu Odunoiki, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Laraba.

Ya bayyana cewa ’yan bindigar sun sace shi ne a lokacin sallar Magariba, inda suka harba bindiga a sararin samaniya yayin da suke tserewa da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!