Connect with us

Labarai

Yan Boko Haram sun kai hari a ƙaramar hukumar Chibok

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan Boko Haram ne sun kai hari a ƙauyen Awapul da ke ƙaramar hukumar Chibok a jihar Borno.

 

Rahotanni sun ce maharan sun shiga yankin ne da misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare, inda suka rika harbe-harbe tare da ƙona gidaje da shaguna.

 

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar, Nahum Daso, ya tabbatar da aukuwar harin, inda ya ce babu asarar rayuka, sai dai an lalata dukiyoyi.

 

Wasu mazauna yankin sun ce maharan sun shafe sama da awa guda suna barin wuta, lamarin da ya tilasta wa mutane da dama tserewa domin samun mafaka.

 

Wannan hari na zuwa ne ƙasa da awa 24 bayan wani makamancin hari da aka kai sansanin ‘yan gudun hijira a Damasak, inda aka kashe jami’an tsaro da kuma lalata dukiyoyi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!