Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Yan fashi sun kaiwa shugaban kungiyar kwadago reshen jihar Benue hari

Published

on

A jiya Talata ne Yan fashi suka kaiwa shugaban kungiyar yan kwadago ta kasa reshen jihar Benue Godwin Anya hari a dai-dai lokacin da kungiyar ke gudanar da zanga-zangar tilastawa fadar shugaban kasa ta aikewa da majalisun tarayyar kasar nan kudurin dokar mafi karancin albashi don mayar da ita doka.

Sai dai kuma ya tsallake rijiya da baya a lokacin da suka kawo masa, amma dai sun harbi matar sa.

Anya da iya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai ta wayar tarho, inda ya tabbatar da cewa harin ne ma ya hana shi halartar taron zanga-zangar da suke aka gudanar a jiya Talata.

Ya kuma kara da harbin matar sa da aka yi ne ya hanashi jagorantar zanga-zangar.

Sai dai kuma hakan bai hana sauran shugabannin kungiyar gudanar da zanga-zangar da suka mamaye manyan titunan babban birnin jihar Makurdi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!