Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shugaba Buhari ya kaddamar da shirin asusun tallafin kula da harkokin lafiya

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya kaddamar da shirin asusun tallafin kula da harkokin lafiya wato Basic Health Care Provision Fund, wanda aka sanya shi cikin kunshin kasafin kudin bana. 

Gwamnatin tarayya dai za ta rika ware kaso daya na dukkan arajin da ake samu da kuma gudunmawa daga kungiyoyin ba da tallafin lafiya a cikin asusun kula da tallafin harkokin lafiyar.

Majalisun dokokin tarayyar kasar nan dai tun a shekarar dubu biyu da goma sha hudu suka yi dokar asusun tallafin kula da harkokin lafiya sai dai sai a wannan karon gwamnatin tarayya ta sanya shi cikin kasafin kudi.

Da ya ke kaddamar da shirin shugaban Buhari wanda ministan kasafin kudi da tsare-tsare Sanata Udoma Udo Udoma ya wakilta, ya ce gwamnatin tarayya ta ware naira biliyan hamsin da biyar da miliyan dari daya don fara shirin asusun tallafin kula da harkokiin lafiya

Haka zalika, gidauniyar fitaccen attajirin nan na Amurka Bill and Melinda Gates Foundation ta ba da dala miliyan biyu domin fara shirin asusun tallafin kula da harkokin lafiyar.

Sauran wadanda suka yi alkawarin ba da gudunmawa cikin asusun tallafin kula da harkokin lafiyar, sun hada da: Cibiyar ba da tallafi ta duniya wadda ta yi alkwarin dala miliyan ashirin, yayin da hukumar bunkasa kasashe ta burtaniya (DFID) ta ce za ta ba da fan miliyan hamsin a cikin asusun.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!