Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

‘Yan garkuwa sun sace dagaci a Kano

Published

on

Masarautar Karaye a jihar Kano ta bayyana cewa wasu masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa sun sace dagacin Karshi dake karamar hukumar Rogo Malam Ado Muhammad Lawan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na masarautar Haruna Gunduwawa, ya fitar a yau Alhamis.

A rahoton da hakimin Rogo Wanban Karaye Alhaji Muhammad Muhammad Mahraz ya gabatar wa Sarkin Karaye Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II ya ce ‘yan garkuwar sun sace shi ne da misalin karfe 2:00 na daren Litinin din da ta gabata   13 ga wannan wata na Janairu.

Sanarwar ta kara da cewa, kimanin mutane 10 ne suka kutsa kai cikin gidan dagacin inda suka fito da shi tare da yin tafiyar kilo mita 10 sannan suka dora shi a kan babur.

Sai dai duk kokarin mutanen garin na kwatarsa ya ci tura sakamakon tarin manyan makaman da bat agarin ke dauke da su.

Tuni dai ‘yan garkuwar suka kira iyalan dagacin ta wayar tarho inda suka fara neman kudin fansa da har yanzu bas u bayyana adadinsu ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!