Labarai
Yan Najeriya 570 aka kashe daga Janairu zuwa Afrilu- NHRC

Hukumar kare haƙƙin Dan-adam ta Najeriya ta ce adadin mutum ɗari biyar da saba’in (570) aka kashe a watan Afrilun bana.
Hukumar, ta bayyana hakan ne ta cikin wani sabon rahoto da ta fitar.
Haka kuma, ta ce, mutane ɗari biyu da saba’in da takwas (278) aka yi garkuwa da su daga alƙaluman da ta tattara, a baya baya nan.
Ta cikin jawabin da ta wallafa a shafinta na intanet, hukumar ta ce, ta tattara alƙaluman ne daga koken da ta samu na keta haƙƙin ɗan adam daga ofisoshinta da ke sassan Najeriya.
Rahoton dai ya yi nazari ne tun daga watan Janairun bana har zuwa watan Afrilu.
You must be logged in to post a comment Login