Connect with us

Labarai

‘Yan sanda a Najeriya sun tsare Alwan Hassan bisa zargin Barau Maliya da hana tabbatar da nadin Ramat a NERC

Published

on

Rahotanni sun bayyana cewa rundunar ’yan sandan Najeriya ta tsare Alwan Hassan kwanaki kaɗan bayan da ya zargi mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, da yin katsalandan wajen hana tantancewa da tabbatar da nadin Abdullahi Garba Ramat a matsayin shugaban Hukumar Kula da Lantarki ta Kasa (NERC).

Wani rahoto daga DAILY NIGERIAN ya bayyana cewa an tsare Alwan Hassan ne a ranar Juma’a bayan ya amsa gayyatar da Sashen Binciken Manyan Laifuka na rundunar (FCIID) da ke Abuja ya aike masa.

A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da bincike kan zargin da Alwan ya yi, tare da tantance tasirin da maganganunsa suka haifar a siyasar jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!