Connect with us

Labarai

Yan sanda sun kama wanda ake zargi da kai wa yan bindiga alburusai a Zamfara

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, ta kama wani mutum da ta ke zargi da safarar alburusai ga yan bindiga tare da samunsa da harsasai masu rai guda 800 da aka boye su a cikin tankin mai na babur.

 

Rundunar ta bayyana haka ne ta cikin wata sanarwa, jami’inta na hulda da jama’a DSP Yazid Abubakar, ya fitar.

 

Sanarwar ta ce, an kama wanda ake zargin mai suna Mannir Adam, mai shekaru 25, mazaunin kauyen Yan-kuzo da ke karamar hukumar Tsafe, a ranar 10 ga watan nan da muke ciki na Maris da misalin karfe 7:50 na dare a kan babban titin Gusau zuwa Funtua a wani shingen binciken ababen hawa.

 

Haka kuma, sanarwar, ta ruwaito cewa, jami’an ‘yan sanda da ke aikin sintiri sun tare wanda ake zargin ne yayin da ya ke tuka babur kirar Boxer mai launin ja, inda bayan bincike suka gano alburusan da aka boye a tankin man babur din.

Rundunar ta kuma bayyana cewa, Binciken farko ya nuna wanda ake zargin na kan hanyarsa ne daga Unguwar Bawa a karamar hukumar Saminaka ta Jihar Kaduna, zuwa kauyen Kucheri da ke karamar hukumar Tsafe a Zamfara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!