Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Yan sanda sun tabbatar da mutuwar mutane 2 a fadowar ginin Anambra

Published

on

Rundunar yan sandan jihar Anambra ta tabbatar da mutuwar mutane biyu sakamakon fadowar wani gini a yammacin jiya laraba a garin Onitsha.

Mai magana da yawun rundunar, Haruna Muhammad ne ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a AwKa babban birnin jihar.

A cewar sanarwa, ginin da ke lamba 9 a kan titin Ezenwa a garin na Onitsha  ya fado ne da misalin karfe 3:00 na yammacin jiya Laraba, kuma mallakin wani mutum ne mai suna Barista Ikebu.

Sanarwar ta kuma ce, tuni ‘yan sanda da masu bada agajin gaggawa suka kai dauki ga wadanda abin ya shafa, kuma an garzaya da su zuwa babban asibitin jihar da ke garin na Onitsha.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!