Connect with us

Labarai

‘Yan ta’adda sun kai mummunan hari a sansanin jami’an Civil Defence

Published

on

Wasu yan ta’adda sun kai hari wani sansanin jami’an tsaro na Civil Defence da ke kauyen Ibrahim Leteh da ke kan hanyar Wawa Lumma a karamar hukumar Borgu ta Jihar Neja 

 

Rahotanni sun bayyana cewa Maharan sun zo su da yawa Inda suka bude wuta kan jami’an tsaron da misalin karfe 4 na safiyar Talata lamarin daya tilastawa wasu daga cikin jami’an tserewa domin tsira da rayuwar su 

 

Jaridar Daily trust ta rawaito cewa yan ta’addan sun tafi da wasu daga cikin bindugu na jami’an Civil Defence din

 

Sai dai mai magana da yawun rundunar tsaron ta Civil Defence a jihar ta Neja Abubakar Rabi’u, ya ce, su na ci gaba da buncike domin har yanzu ba su tantance gaskiyar abinda ya faru ba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!