Labarai
Yanzu -yanzu : Gwamnan Ekiti ya kamu da cutar Corona
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/07/114ff3fa-kayode-fayemi.jpg)
Gwamnan jihar Ekiti Dr. Kayode Fayemi ya sanar da cewa ya kamu da cutar corona.
Hakan na cikin wata sanarwar ce da gwamnan ya wallafa a shafin sa na Twatter a yau Laraba.
A cewar Kayode Fayemi wanda shine shugaban kungiyar gwamnonin kasar nan ya ce shi ne karo na uku da aka yi masa gwajin cutar kuma a wannan karon sakamakon ya nuna cewa yana dauke da kwayar cutar ta covid-19.
Gwamnan na jihar Ekiti ta cikin sanarwar ya ce, tuni ya dauki matakin killace kansa tare da samun kulawar jami’an lafiya.
You must be logged in to post a comment Login