Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zaɓen 2023: INEC ta sanar da ranar zaɓen shugaban ƙasa da gwamnoni

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta ayyana 25 ga watan Fabrairun 2023 a matsayin ranar zaɓen shugaban ƙasa.

Shugaban hukumar na Farfesa Mahmud Yakubu ne ya sanar da hakan a wani taron manema labarai a Abuja ranar Asabar.

Farfesa Yakubu ya ce a yanzu za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar 25 ga Fabrairun 2023, yayin da za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisun jihohi a ranar 11 ga Maris ɗin 2023.

Farfesa Yakubu ya bayyana cewa tsayar da ranar akan lokaci zai ba ba da damar yin shirye-shirye a kan lokaci daidai da tanade-tanaden dokokin zaɓe wadda ta ce, a bada sanarwar zaɓe akalla kwanaki 260 kafin zaɓen.

Shugaban na INEC ya kuma ce za a sanar da ƙa’idojin zaɓen a nan gaba Kaɗan.

#Solacebace

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!