Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za mu tallafawa kamfanonin da suka durkushe a Kano – Gwamnati

Published

on

Ministan ciniki, kamfanoni da zuba jari Otunba Niyi Adebayo ya ce gwamnatin tarayya zata tallafa wajen farfado da kamfanoni da suka durkushe  a jihar Kano, kasancewar su ne ginshikai wajen bunkasa tattalin arzikin kasar nan, bayan da annubar cutar COVOID-19 ta kawo koma a wannan bangaren tattalin arzikin kasar nan.

Mr Otunba Adebayo ya bada tabbacin ne lokacin da ya kai ziyarar girmamawa ga mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a fadar sa.

Ministan wanda ya sami wakilcin babban darakatan tsare-tsare na ma’aikatar Alhaji Tijjani Inuwa Babura ya ce sun zo Kano ne don tantance adadin kamfanonin da annubar Korona ta yi wa illa, da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki don samu bakin-zaran don tallafawa masu kamfanoni a nan Kano.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!