Connect with us

Labarai

Za mu yi duk mai yiwuwa wajen kawo karshen fadan Daba- Inuwar Kofar Mata

Published

on

Kungiyar Inuwar Kofar Mata da ke jihar Kano, ta ce, za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin an kawo karshen fadan Daba, da ake samu Musamman tsakanin Unguwannin Kofar Mata da Yakasai da kuma Zango, ta hanyar samar wa da mata da matasan yankunan ayyukan yi.

 

Kungiyar, ta bayyana haka ne yayin da ta ke bikin bude cibiyar koyar da matasa sana’o’in dogaro da kai  ga matasa a yankin da ya gudana a Larabar makon nan.

 

A jawabinsa yayin taron, Shugaban Kungiyar ta Inuwar Kofar Mata, Alhaji Adamu kofar Mata, kira ya yi ga iyaye da su yi amfani da wannan dama  wajen tura yayan su domin su dogara da kansu.

 

Shi kuwa Mai Unguwar Kofar Mata Malam Muhammad Jibrin Muhammad, ya yi fatan samar da cibiyar zai kawo karshen rashin aikin yi  da shaye-shayen da matasan yankin ke fama da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!