Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zamfara:rundunar yan sanda ta musanta rahotannin kai hari ga shaidun Atiku Abubakar

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta musanta rahotannin da ke cewa an kai hari ga wasu shaidun dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar.

 

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in yada labaran Hukumar SP Muhammed Shehu.

 

Sanarwa ta ce babu kanshin gaskiya cikin zargin cewa an kai hari ga shaidun dan takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubakar a jihar ta Zamfara.

 

Tun farko dai lauyan Atiku Abubakar ya shaidawa kotun sauraran korafin zaben shugaban kasa a zamanta na karshen makon jiya cewa, an kai hari ga wasu shaidun su wadanda suka bar jihar Zamfara akan hanyarsu ta zuwa Abuja.

 

Lamarin da ya sa alkalan kotun sauraran korafin zaben shugaban kasar, su ka dage ci gaba da sauraran karar zuwa wani lokaci nan gaba.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!