Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zan daure duk Bafulatani da ya kafa kungiyar tsaro a Benue – Samuel Ortom

Published

on

Gwamnan jihar Benue Samuel Ortom ya ce zai tabbatar duk wani Bafulatani makiyayi da yayi yunkurin kafa kungiyar tsaro ta Vigilante ya daure shi.

Wannan na zuwa ne biyo bayan taron manema labarai da kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore ta gudanar a birnin tarayya Abuja kan yadda za a magance matsalolin tsaro a jihar.

Sai dai a martanin sa ta bakin sakataren yada labaran sa Terver Akase, Samuel Ortom ya gargadi kungiyar Fulanin da su kada suyi gaggawar kafa rundunar tsaron Vigilante.

A cewar sa za su yi amfani da wannan damar wajen aiwatar da wasu muggan dabi’u da za su kawo rashin zaman lafiya a sassan jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!