Connect with us

Labarai

Zan nemi takarar shugaban ƙasa a 2027 don kawo ƙarshen mulkin APC- Peter Obi

Published

on

Ɗan takarar jam’iyyar Labour Party LP a zaben shekarar 2023 Peter Obi, ya ce zai nemi takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027 domin kawo ƙarshen mulkin APC.

 

Da ya ke magana ta cikin shirin Sunday Politics na gidan Talabijin na Channels, Peter Obi, ya ce ba su taɓa yin magana da wani ba kan cewa zai yi masa mataimaki a takarar.

 

Haka kuma Peter Obi ya kuma tabbatar da cewa har yanzu ɗan jam’iyyar Labour ne shi duk da cewa yana cikin jam’iyyar haɗaka ta ADC da ta ƙunshi sauran jagororin adawa da za su ƙalubalanci Shugaba Bola Tinubu na APC a 2027.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!