Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zargin juyin mulki: Sojoji a Mali sun tsare shugaban kasa, firaminista, ministan tsaro

Published

on

Rahotanni daga kasar Mali na cewa sojoji sun kama shugaban rikon kwarya na kasar Mali Bah Ndaw da firaministan kasar Moctar Ouane.

 

Haka zalika sojojin sun kuma kama ministan tsaron kasar Souleymane Doucoure.

 

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa, an tsare mutanen uku ne a sansanin soji da ke Kati wani gari da ke da nisan kilomita goma sha biyar daga arewa maso yammacin birnin Bamako.

 

Wannan juyin mulki na zuwa ne jim kadan bayan da gwamnatin rikon kwarya na kasar ta gudanar da garambawul ga majalisar ministocin kasar.

 

A watan Agustan bara ne sojoji suka kifar da gwamnatin shugaba Ibrahim Boubacar Keita sakamakon rikicin siyasa da ya kaure a kasar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!