Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zargin safarar ƙwaya: NDLEA na neman DCP Abba Kyari Ruwa a jallo

Published

on

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa NDLEA, ta ce tana neman dakataccen kwamandan sashin yaƙi da miyagun ayyuka da ke aiki a ofishin babban sufeton ƴan sandan ƙasar nan DCP Abba Kyari ruwa a jallo.

Neman nasa dai ya biyo bayan zargin sa da hannu a cinikin hodar Iblis da nauyinta ya kai kilogiram 25.

Hukumar NDLEA ta bayyana Kyari a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo a wani taron manema labarai da daraktan yaɗa labaranta Femi Babafemi ya gabatar a shelkwatarta da ke Abuja a ranar Litinin 14 ga Fabrairu, 2022.

Hukumar ta ce, ta ɗauki matakin ne bayan ƙoƙarin da ta yi na gayyatar sa domin amsa tambayoyi amma hakan ya ci tura.

NDLEA ta kuma tabbatar da cewa DCP Kyari na cikin mambobin ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi daga ƙasashen Brazil da Ethiopia zuwa Najeriya, a don haka yana buƙatar ya amsa tambayoyin daga hukumar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!