Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NDLEA ta kama dan kasar Chadi da ake zargin yana safarar kwayoyi ga Boko haram

Published

on

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta kama wani mutum dan asalin kasar Chadi mai suna Adama Oumaru Issa wanda ake zargin yana safarar miyagun kwayoyi ga kungiyar boko haram.

Mutumin mai shekaru talatin da biyar an kama shi ne a garin Jalingo da ke jihar Taraba.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA Femi Babafemi, ya ce, binciken su na farko ya gano cewa, mutumin dillali ne da ya kwarance wajen safarar miyagun kwayoyi ga ‘yan boko haram da ke bakin daga.

A cewar sa, wanda ake zargin ya kuma sayo kwayoyin ne a garin Onitsha da ke jihar Anambra, inda ya boye su cikin jakar mata.

Ya kuma ce dubun sa ya cika ne a lokacin da ya ke kan hanyar sa ta kai miyagun kwayoyin ga ‘yan boko haram.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!