Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Ƙalubale 10 da bangaren ilimi a Kano ke fuskanta

Published

on

Mai sharhi kan al’amuran ilimi kuma malami a tsangayar ili a jami’ar Bayero da ke nan Kano ya bayyana tsarin ilimi kyauta kuma dole da gwamnatin Kano ta fito da shi a matsayin abinda bai tasiri ba.

Dakta Idris Salisu Rogo ne ya bayyana hakan ta cikin shirin “Duniyar mu a yau” na nan Freedom Radio.

Rago ya ce “tun bayan ayyana tsarin ilimi kyauta shekaru biyu da suka gabata, gaba ɗaya harkar ilimi ta sake lalacewa musamman a matakin Firamare”.

Dakta Rogo ya lisaffa ƙalubale 10 da bangaren ilimi ke fuskanta a jihar Kano kamar haka:

1- Har yanzu gwamnati ba ta san walwalar malaman makaran ta ba.

2- Rashin kayan aiki ga malamai.

3- Rashin kyakyawan muhallin karatu ga ɗalibai da malamai.

4- Rashin tura malamai karo karatu don ƙwarewa.

5- 3 Rashin ɗaga likkafar malamai zuwa mataki na gaba wato Promotion.

6- Rashin kyakyawan albashi.

7- Ɗaukar malamai marasa kwarewa a fannin.

8- Rashin samar da wadatattun malamai a makarantu.

9- Rushe tsarin Zonel Office wanda su ke bibiyar makarantu.

10- Rashin samar da shugabanci mai kyau a makarantu.

Rogo ya ce, matukar aka ci gaba da tsarin bada ilimi kyauta koma dole to kuwa harkokin ilimi zai shiga cikin mawuyacin hali.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!