Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ilimi kyauta kuma dole ya haifar da cinkoson dalobai a Kano – SUBEB

Published

on

Hukumar ilimin bai daya ta jihar Kano SUBEB ta ce, shirin bada ilimi kyauta kuma dole ya haifar da cinkoson dalibai a makarantun Firamare a Kano.

Shugaban hukumar Dakta Danlami Hayyo ne ya bayyana hakan a zantawarsa da Freedom Radio.

Tattaunawar ta mayar da hankali kan kaluablen da harkokin ilimi ke fuskanta a yanzu.

Dakta Danlami Hayyo ya kuma ce, batun korafin da wasu malamai suke yi na rashin yi musu karin albashi yana da alaka da rashin basu takardar karin girma a rubuce.

Da yake batu kan shagunan da ake ginawa a jikin makarantu’ Danlami Hayyo ya ce “Da zan samu ikon zama gwamna na yini daya a Kano da duk sai na rushe shagunan da aka gina a jikin makarantun”.

Wannan dai na zuwa ne yayin da ilimin Firamare ke ci gaba da fuskantar kalubale.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!