Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan adaidaita sahu su koma bakin aikinsu – Sani Ɗan koli

Published

on

Ƙungiyar ƴan adaidaita sahu a jihar Kano ta buƙaci mambobinta da su koma bakin aikin su daga yanzu.

Shugaban ƙungiyar a jihar Kano Alhaji Sani Sa’idu Ɗan Koli ne ya tabbatar da hakan ga Freedom Radio da yammacin ranar Talata.

Ɗan koli ya ce “Bayan umarnin majalisar dokokin jihar Kano yanzu haka mun kammala ganawa da hukumar DSS wadda ta bamu tabbacin janye yajin aiki”.

“DSS ta sanar da mu cewa gobe Laraba da ƙarfe 10 na safe za mu ji kyakkyawan labari don haka daga yanzu kowanne mai adaidaita sahu zai iya fita domin ci gaba da kasuwancinsa”.

Ɗan Koli ya kuma ce, yana mai bai wa direbobin babura masu ƙafa uku tabbacin cewa matsalolin su sun zo ƙarshe.

Wannan dai na zuwa ne bayan da shugaban majalisar dokokin jihar Kano Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari ya buƙaci ƙungiyar ƴan adaidaita sahun da su janye yakin aikin da suke domin kuwa za su shiga tsakani don sulhuntawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!