Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ganduje ya sassauta dokar daukan mutum daya a baburin adaidaita sahu

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta sassauta dokar da ta sanyawa ‘yan Adaidaita sahu ta daukar fasinja daya tilo bayan sake nazartar dokar, inda ta ce yanzu fasinjoji biyu za su rinka dauka amma ko wannensu da abin rufe hanci, don kare kai daga cutar Covid-19.

Shugaban hukumar kula da ababen hawa ta Jihar Kano KAROTOA Baffa Babba-Dan-Agundi ne sanar da hakan, inda ya ce matakin sassauta dokar ya biyo-bayan ganawa da kwamishinan sufuri na Jihar Kano Barista Muhammad Lawal da sauran masu ruwa da tsaki.

Zamu fara kama baburan Adaidaita sahu -KAROTA

Ya kara da cewa sauran masu motocin haya ma dokar ta shafe su inda aka rage muku yawan fasinjojin da suke dauka, sannan kuma wajibi ne su samar da sinadarin tsaftace hannu a cikin abin hawan na su.

Baffa Babba Dan-Agundi ya shaida cewa gamayyar tsaro da kungiyoyin masu motocin haya da na Adaidaita sahu ne za su yi aikin tabbatar da bin dokar, karkashin jagorancin kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano.

Haka zalika ya gargadi jama’a wajen ganin sun mutunta dokar, domin ko duk wanda aka kama da laifin karya doka zai fuskanci hukunci daidai da abinda ya aikata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!