Connect with us

Labarai

Ƴan bindiga sun afka wa tawagar gwamnatin Zamfara

Published

on

Rahotanni daga jihar Zamfara na cewar ƴan bindiga sun buɗe wuta ga tawagar da gwamnatin jihar ta aika zuwa Katsina.

Farmakin yayi sanadiyyar rasa ran mutum guda.

Hakan na cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na ƴan sandan jihar SP Shehu Muhammad ya fitar a daren Litinin.

Tawagar ta je Katsina ne domin miƙa ƴan mata 26 da aka kuɓutar daga ƴan bindiga ga gwamnati.

Labarai masu alaƙa:

Da ɗumi-ɗumi: An ceto ƴan mata dagahannun ƴan bindiga a Zamfara

Gwamnatin Katsina ta karɓi ƴan matan da aka kuɓutar a Zamfara

Sanarwar ta ce, yanzu haka ƴan sanda sun shiga bincike kan lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!