Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Katsina ta karɓi ƴan matan da aka kuɓutar a Zamfara

Published

on

Gwamnatin jihar Katsina ta karɓi ƴan mata 26 da aka kuɓutar daga ƴan ta’adda a hannun gwamnatin Zamfara.

Gwamnan jihar Aminu Bello Masari ne ya karɓi ƴan matan a daren Lahadi a fadar gwamnatin jihar.

“babu sauran sassauci ga duk ƴan bindigar da ke hallaka mutane a yankunan jihar” a cewarsa.

Gwamnan ya kuma yi godiya ga gwamnatin Zamfara kan kuɓutar da ƴan matan.

Gwamna Aminu Bello Masari bayan ya karbi ‘yan matan da aka kubutar daga hannun ‘yan bindiga

Kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na Zamfara Abubakar Justice Dauran ne ya jagoranci tawagar miƙa ƴan matan.

Ya ce, “Gwamnati ta samu nasarar kuɓutar da ƴan matan ne ta hanyar bayanan sirri da tubabbun ƴan ta’adda suka bayar”.

Ƴan mata 26 da aka kuɓutar daga ƴan bindiga a Zamfara

Dauran ya ƙara da cewa, Gwamnan Zamfara ya ɗinka musu kaya saboda mafi yawa an same su tsirara.

Sannan gwamnan Zamfara ya bai wa kowacce kyautar Naira dubu goma-goma.

Labarai masu alaka

Da ɗumi-ɗumi: An ceto ƴan mata daga hannun ƴan bindiga a Zamfara

Zamu hukunta duk basaraken da ya fita daga Zamfara – Matawalle

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!