Connect with us

Labarai

Ƴan bindiga sun hallaka Hakimin garin Dogon Daji

Published

on

Wasu ƴan bindga ɗauke da makamai sun afka wa garin Dogon Daji da ke yankin ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, tare da hallaka hakimin garin.

 

Shugaban ƙaramar hukumar Tsafe Garba Shehu Tsafe ya tabbatar wa BBC cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Litinin.

 

Ya ƙara da cewa a wunin ranar ƴanbindigar sun tare wasu hanyoyi a yankin da ke kai wa zuwa Gusau.

 

Shugaban ƙaramar hukumar ya alaƙanta ƙaruwar hare-haren yankin da sluhun da ake yi a jihar Katsina mai makwabtaka.

 

Ko da a baya bayan nan dai Rahotanni daga karamar hukumar Kanam da ke Jihar Filato na nuna cewa an samu gawar Sarkin Ƙauyen Shuwaka, Mallam Hudu Hassan Barau, wanda ’yan bindiga suka sace kusan mako guda da ya wuce.

 

Malam Hudu, wanda shi ne Dagacin Shuwaka a gundumar Kyaram, cikin al’ummar Garga, an gano gawarsa ne bayan kwanaki shida da ’yan bindiga suka yi awon gaba da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!