Connect with us

Labarai

Ƴan bindigar da suka sace ɗalibar BUK sun buƙaci miliyan 100 kuɗin fansa

Published

on

BUK 92 Class

Ƴan bindigar da suka sace ɗalibar jami’ar Bayero mai suna Sakina Bello sun nemi kuɗin fansa na naira Miliyan ɗari kafin sakin ta, kamar yadda jaridar daily trust ta rawaito.

Tun a ranar Talata ne ƴan bibdigar suka sace ɗalibar da misalin ƙarfe uku na yamma a cikin baburin adaidaita sahu, tsakanin unguwar Janbulo da Rijiyar Zaki jim kaɗan bayan fitowarta daga gida.

Sakina ɗaliba ce mai shekaru 23 a tsangayar nazarin harkokin lafiya { Botany} kuma tana shekara ta uku a karatun ta.

Ƴan bindigar dai sun kira ɗan uwan Sakina da misalin ƙarfe 9 na dare ranar tare da tabbatar da cewa sune suka ɗauke ta, a don haka za su kira ranar laraba.

Sai dai rundunar  ƴan sandan jihar kano ta tabbatar da sace ɗalibai ta bakin mai magana da yawunta DSP Abdulahi Haruna Kiyawa.

Kiyawa ya ce, su na ƙoƙarin ganin an kuɓutar da Sakina Bello nan ba da jimawa ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!