Connect with us

Labarai

Ƴan sanda sun ceto mutane 10 da aka sacesu a Kagarko

Published

on

Rundunar ƴan Sandan jihar Kaduna, ta ce, jami’anta sun ceto mutane 10 da aka sace a yankin Kagarko na Jihar Kaduna.

 

Mai magana da yawun rundunar, DSP Mansir Hassan, ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Kaduna.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, wasu ƴan bindiga kimanin 14 sun kai hari a ƙauyen Kushe Makaranta da ke ƙaramar hukumar Kagarko, inda suka sace wasu mazauna yankin suka tafi da su cikin dajin Rijana.

 

Rundunar ta ce bayan samun matsin lamba daga jami’an tsaro, ’yan bindigar sun tsere sun bar wadanda suka sace ɗin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!