Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan sanda sun ceto mutane 187 daga hannun masu garkuwa da mutane

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta miƙa sama da mutane 187 a hannun gwamnatin jihar, bayan sun kuɓutar da su daga masu garkuwa da mutane.

Mai magana da yawun rundunar Muhammad Shehu ne ya bayyana hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, waɗanda aka ceto din sun haɗar da mata da maza har ma da ƙananan yara a cikin su.

Shehu ya kuma ce, bayan wasu ayyuka na musamman da aka gudanar a dajin Tsibiri da ke ƙaramar hukumar Maradun, an gano mutanen da aka yi garkuwa da su a ƙauyukan Rini, Gora, Sabon Birni da Shinkafi a ƙananan hukumomin Bakura Maradun da kuma Shinkafi.

A cewar sanarwar tuni kwamishinan ƴan sandan jihar Ayuba Elkanah ya miƙa waɗanda aka ceto ga gwamna Muhammad Bello Matwalle, inda ya tabbatar masa cewa za a ci gaba da bincike.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!