Connect with us

Ƙetare

Ƴan sandan London sun tarwatsa waɗanda ake zargi da fashin Wayoyi

Published

on

Ƴan sanda a birnin London sun ce, sun tarwatsa wata ƙungiyar barayi ta ƙasa da ƙasa da ta kware wajen safarar wayoyin salular jama’a da suka kwashe kimanin  40,000 tare da kai su zuwa China.

Magajin garin birnin Sadiq Khan, ya ce, ƴan sanda sun dirar wa shugabannin masu aikata laifukan ne ciki har da masu ƙwacen waya a kan tituna.

Aƙalla mutane 16 aka kama, a binciken da aka kwashe shekara guda ana yi.

Wakiliyar BBC ta ruwaito cewa, tuni aka gurfanar da mutane uku, ciki har da ƴan Afghanistan da ake zargi da hannu a lamarin.

Haka kuma ta ƙara da cewa, ana tunanin suna sayar da kowacce waya guda ɗaya a kan kusan dalar Amurka 5000 saboda a buɗe suke, saɓanin wayoyin da ake sayarwa a China.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!