Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NAHCON za ta fara hukunta masu karbar kudi fiye da kima a wurin maniyyata

Published

on

Hukumar aikin hajji ta Najeriya NAHCON ta bayyana shirin da take yi na soma hukunta hukumomin jin daɗin alhazai a jihohin ƙasar, da ke karɓar fiye da kuɗin kujerar hajj da hukumar hadin gwiwa da hukumomin suka ƙayyade.

Cikin sanarwa da mataimakin daraktan yaɗa labarai na hukumar ta NAHCON, Musa Ubandawaki ya sanyawa hannu, hukumar ta ce kuɗin hajjin bana da ta sanar ranar Juma’ar da ta gabata bai sauya ba.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa har yanzu farashin kujerar Hajji tana kan ƙasa da naira miliyan uku.

Sanarwar ta kuma gargaɗi duk wata jiha da ke tatsar maniyyatanta, za ta iya rasa lasisinta ko ma rasa kason kujerun hajjin da aka ware mata ba tare da ɓata lokaci ba.

Rahoton: Ahmad Kabo Idris

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!