Connect with us

Labarai

PDP ta kafa kwamitin da zai magance mata rikicin cikin gida

Published

on

Jam’iyyar adawa ta PDP, ta kafa kwamitin da zai kawo ƙarshen matsalar rikicin cikin gida da ta ke fuskanta.

 

Jam’iyyar ta bayyana daukar wannan mataki ne bayan gudanar da taron masu ruwa da tsaki, da ta gudanar a baya-bayan nan.

 

Wannan lamari dai na faruwa ne yayin da Ministan birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike ke ƙalubalantar jam’iyyar wajen bayar da tikiti a shiyyar Arewacin kasar nan.

 

Wannan dai na zuwa ne yayin da bangaren dan takarar shugabancin ƙasa na jam’iyyar a zaben shekarar 2023 Atiku Abubakar ke zargin cewa akwai wasu gwamnoni da suke taka rawa wajen goya wa Minista Wike baya, wajen  haddasa rikicin cikin gida a jam’iyyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!