Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kwalejin Kimiyya dake Dawakin Kudu ta samar da sabon dakin kwanan dalibai

Published

on

Daraktan kwalejin kimiyya dake Dawakin Kudu Malam Abdullahi Musa Gezawa, ya bukaci masu hannu da shuni da sauran mutane da su himmatu wajen bayar da gudunmawa don ci gaban ilmi.

Malam Abdullahi Musa Gezawa ya bayyana hakan ne yayin bada kyaututtuka ga dalibai da malamai da suka yi hazaka a kwalejin.

Ya ce hukumar kwalejin tuni tayi shiri kan hanyoyin da za a dawo da cikakken tsarin koyarwar ilmin kimiyya ga dalibai.

Malam Abdullahi Musa Gezawa ya kuma kara da cewa, sashen jagoranci da nusarwa na kwalejin kimiyya ta Sani Bello dake Dawakin Kudu ya mai da hankali wajen gyara dabi’un dalibai don haifar da al’umma ta gari.

Da yake jawabi tun da faru, shugaban jami’ar Kimiyya da Fasaha dake garin Wudil Farfesa Shehu Alhaji Musa ya hori daliban da jajircewa kan karatun su, duba da ci gaban kowacce kasa ya ta’allaka ga ilmin kimiyya.

An fara amfani da sabon dakin kwanan dalibai mai cin mutane 80 da kungiyar tsoffin daliban kwalejojin kimiyya KASSOSA ta gina domin rage yawan dalibai a sauran dakunan kwanan su, da kuma samar da sabon masallaci tare da daukar gabaran gyara dakunan gwaje-gwajen na kwalejin da kungiyar ta dauki nauyi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!