Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin Kano zata kirkiro sababbin sarakunan gargajiya

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci kwamitin ta da ke kula da kananan hukumomi da sarautun gargajiya da ya dauko dokar sarautar gargajiya ta jihar ta Kano domin nazarin kan yiwuwar kafa sabbin sarakunan yanka masu daraja ta daya a jihar.

Hakan ya biyo bayan karanta wata wasika da wani ofishin lauya mai suna Ibrahim Salisu chambers ya aikowa majalisar; wanda ya bukaci kafa sabbin masarautu a kananan hukumomin Rano da Gaya da Karaye da kuma Bichi.

Yayin tattauna batun mabobin goma sha uku da suka bada gudunmawa sun goyi bayan dauko dokar domin nazarin ta a gobe Talata.

Sai dai ya yin zaman majalisar na yau mamba mai wakiltar karamar hukumar Gezawa Isyaku Ali danja ya fice daga zauren, yana mai zargin takwarorinsu da sa siyasa cikin lamarin.

Da ya ke kare matakin da suka dauka kan batun, shugaban masu rinjaye na majalisar Baffa Babba Dan-Agundi ya ce babu batun siyasa cikin Matakin da suka dauka.

majalisar ta umarci kwamitin da ya kawo dokar a gobe talata.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!