Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kamfanin TCN ya ce wasu kwantenoninsa guda biyu sun yi batan dabo

Published

on

Kamfanin tunkudo wutar lantarki na kasa TCN ya ce wasu kwantenoninsa guda biyu da ke dauke da kayayyakin lantarkin sun yi batan dabo a wasu tashoshin jiragen ruwan kasar nan.

Manajan darakta kamfanin na TCN Usman Gur Muhammad ne ya bayyana hakan a jiya Laraba yayin zantawa da manema labarai a Abuja, yana mai cewar guda daga cikin kwantenoni 775 da aka gano babu komai a cikinta.

Usman Gur ya shaida cewa kamfanin ya cimma matakin karfin lantarki da Yammacin Afirka da aka tsayar, kuma yana kan hanyarsa kara bunkasa wutar da akalla megawatt 2000 zuwa 3000.

Ya kuma kara da cewa duk da dimbin jarin da kamfanin ke zubawa tare da tunkudo wutar, to amma kamfanonin rarraba wutar wato DisCos sun gaza wajen daidaituwa da TCN din musamman fannin inganta kayayyakin aikinsu.

Kuma hakan na kawo nakasu ga samar da isasshiyar wutar lantarkin a kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!