Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Kamfanin TCN ta tallata gwanjon jirage masu saukar ungulu

Published

on

Jirgi mai saukar ungulu

Bayan shafe shekaru na halin ko in kula da kamfanin samar da  wutar lantarki ta kasa ,wanda ta gada daga tsohowar kamfanin wutar lantarki NEPA na wasu  jirage masu saukar ungulu guda hudu, wanda kudadensu ya kai kimanin dala dubu dari bakwai da ashiri kwatankwacen fiye da Naira miliyan dari biyu da hamsin da biyu, wanada za’a yi gwanjon  su.

 

Jiragen mallakin hukumar samar da wutar lantarki ta  sun bayyana kudirinsu na gwanjon wadannan jirage mai kirar BO-105 , da suke ajeye a filin jiragen saman na cikin gida dake Murtala Muhammad a jihar Lagos.

 

Jaridar Punch ta rawaito cewar jiragen saman masu saukar ungulu da ake amfani da su wajen kai kawon duba kayyakin wutar lantarki tare da aiwatar da wasu gyare-gyare a fadin kasar nan , suna nan zaune ne ba tare da ana amfani da su ba na tsawon lokaci.

 

Biyu daga cikin jiragen masu dauke da lamba 5N-ASK da 5N-ASJ rabon da suyi yi aiki tun a shekara ta 1995-1997, kuma an kira su ne a  shekara 1978.

Kamfanin TCN ya ce wasu kwantenoninsa guda biyu sun yi batan dabo

Kamar yadda hukumar samar da wutar lantarkin  ta ce, babu fa’ida na a gyara su, mai makon haka, kamata yayi a sayar da su a akan kudi dala dubu dari a halin da suke ciki.

 

Ragowar jiragen kuwa guda biyu masu lambar ta rijista 5N-BCj da 5N-EPA suna ajeye ne tun shekara ta 2008 kuma za’a iya sayar da su a kan kudade dala dubu dari uku da arbain da kuma dala dubu dari da tamanin.

 

Su kuma an kira su ne a shekara ta 1996 da kuma 1993 suma gyara wanda za’a iya gyara su domin suyi aiki amma na dan lokaci.

 

Hukumar dai a ‘yan kwanakin nan ne suka fitar da gayyatar masu saye domin su zo su saye.

 

A dai kwanakin baya ne  tawagar gwamnati daga  bangaren sharia suka je suka duba jiragen masu saukar ungulu a ranar Asabar din da ta gabata domin duba su kafin a fara gwanajan su.

 

Haka zalika Shugaban  kwamitin majalisar datijjai dake kula da wutar lantarki sanata Yusuf Yusuf dake wakiltar Taraba ta tsakiya ya ce makasudin ziyarar shi ne  domin duba lafiyar jiragen  kafin a sayar da su.

 

Ya kara da cewa daga cikin abinda suka gani za’a yi iya gwanjon biyu daga cikin su , amma ragowar kuwa za’a iya sayar da su a matsayin ‘yan gwangwan

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!