Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Iyayen yaran da aka sace sun bukaci taimakon al’umma

Published

on

Iyayen yaran da aka sace a sassan uguwannin Hototo da kewaye a nan Kano sun bukaci al’umma da su taya su da addu’ar neman Allah ya bayyana sauran yaran da har yanzu ba a kai ga gano su ba Onitsha ta jihar Anambra.

A cewar wasu daga cikin iyayen yaran yara 49 ne suka bata inda zuwa yanzu aka gano 9 daga cikin su a garin Onitsha na jihar Anambra, bayan da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta jagoranci wani aiki ne nemo yaran.

A zantawar Freedom Radio da Sakataren kungiyar iyayen yaran da ake zargin an sace din Attajiri Hotoro, ya bayyana cewa yanzu haka suna da kalandar hotunan yaran da suka batan su 49 inda ya kara da cewa yanzu haka akwai maganar cewa za a koma domin sake lalubo sauran yaran.

Shi kuwa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Malam Ahmad Iliyasu, ya bayyana cewa sun fara binciken ne kan wani mai suna Paul da aka kama da wani karamin yaro yana yunkurin ficewa da shi daga jihar Kano.

Kwamishinan ya kara da cewa, bayan sun matsa shi da tambayoyi ne ya shaida musu inda suke kai yaran.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!